Alhaji Idris ya ce Ministan ya yi hobbasa wajen ganin wanan aiki ya fara kuma ya yi tsayin daka akan ganin an kammala aikin kafin shekara mai zuwa saboda a cika wa shugaba Buhari burin sa na samar wa kasar da isassar wutar lantarki da akalla mutane miliyan 60 za su mora akai-akai.
Madakin Jen ya ce za a yi wannan aikin ne a karkashin shirin Shugaban kasa da ake kira PPI inda Najeriya za ta wakilci kamfanonin raba hasken wuttar lantarki da sauran masu ruwa da tsaki wajen saka hannun jari, wani abu da shugaban kungiyar Habbaka Matasan Arewa Imrana Nas ya ce an dade ana irin wannan alkawarin amma har yanzu akan batun wutar lantarki ta na kasa ta na dabo, inda ya bada tarihin cewa tun a shekarar 1999 ne ake gwagwagwa tsakanin mahukunta da yan kasa akan lamarin.
Shi ma mai fashin baki a al’amuran yau da kullum Comred Isa Tijjani ya ce in dai ba aikin aka yi aka gama ba, shi ba zai amince da romon baka ba, domin an dade ana ruwa kasa ta na shanyewa a kan batun samar da wutar lantarki.
Abin jira a gani shi ne yadda samar da wutar lantarkin zai kai ga farfado da masana’antun kasar da suka dade a kwance babu motsi.