Ƴanta’adda Sun Yi Awon-gaba Ɗalibai a Wata Makaranta A Borno



Wasu da ake zargin ‘yan ta’adda ne sun sace adadin ɗalibai da ba a tantance ba daga makarantar Mussa Primary da Junior Secondary School da ke ƙauyen Mussa a ƙaramar hukumar Askira/Uba ta jihar Borno.

Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne da safiyar Juma’a yayin da ake gudanar da darussa a makarantar.

Wani malami a makarantar ya shaida cewa maharan sun isa ne kan babura kafin su yi awon gaba da ɗaliban.

Ya ce wasu daga cikin ɗaliban sun samu tserewa zuwa cikin daji, amma da dama an tafi da su.

Dan majalisar tarayya mai wakiltar Askira-Uba/Hawul, Midala Balami, ya bayyana harin a matsayin abin takaici tare da kira ga jami’an tsaro su gaggauta ɗaukar mataki.

Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, rundunar ‘yan sandan jihar Borno da sojoji ba su fitar da wata sanarwa a hukumance kan lamarin ba.

Sace ɗalibai daga makarantu na ci gaba da zama babbar barazana ga tsaro a wasu sassan Arewacin Najeriya, inda masu ɗauke da makamai ke kai hare-hare domin neman kuɗin fansa.

More from this stream

Recomended