Ƴan Sanda Sun Kama Wasu Mutane Biyu Da Ake Zargi Da Yiwa Yarinya Ƴar Shekara 13 Fyaɗe

Jami’an ƴan sanda na rundunar ƴan sandan jihar Gombe sun kama wasu mutane biyu  da ake zargi da yiwa wata yarinya ƴar shekara 13 fyaɗe a wata gona dake garin Bajoga a ƙaramar hukumar Funakaye ta jihar.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ƴan sandan jihar,ASP Mahid Abubakar shi ne ya bayyana haka lokacin da yake nuna mutanen a gaban ƴan jaridu a Gombe.

Abubakar ya bayyana Yayaji Muhammad mai shekaru 24 da kuma Muhammad Barau mai shekaru 20 a matsayin mutanen da aka kama ake kuma zarginsu da aikata laifin.

Ya ce an kama su ne biyo bayan korafi da wani mai suna Mallam Jauro mahaifin yarinyar ya shigar gaban rundunar.

More News

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani ɓangare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...

Matatar Mai Ta Kaduna Za Ta Fara Aiki A Ƙarshen 2024

Kamfanin Kaduna Refining and Petrochemical Company KPRC ya ce matatar mansa za ta fara aiki a shekarar 2024. Mustapha Sugungun managan matatar man ta KRPC...

Manyan dillalan mai za su fitar da litar man fetur miliyan 300 a wannan makon

Ƙungiyar MEMAN ta manyan dillalan man fetur da dangoginsa ta ce mambobinta sun fara lodin mai har lita miliyan 300 a cikin makon nan...

Kotu ta ɗaure mutumin sa ya yi sama-da-faɗi da kuɗin marayu

Babbar kotu a jihar Borno ta yanke wa Isiyaku Ibrahim hukuncin shekara ɗaya a gidan yari da zaɓin biyan tarar naira dubu 100 saboda...