Ƴan Fashin Daji Sun Kashe Wani Fitaccen Ɗan Kasuwa Tare Da Yin Garkuwa Da Ƴarsa Da Matarsa A Jihar Katsina

Ƴan fashin daji  sun kai farmaki ƙauyen Mairuwa dake ƙaramar hukumar Faskari ta jihar Katsina ranar Asabar da daddare dai-dai lokacin da ake gudanar da Sallar Tarawih.

A kalla mutane biyu aka harbe s har lahira a yayin da mutum guda kuma ya jikkata.

Ɗaya daga cikin mutanen da aka kashe, Alhaji Lado fitaccen ɗan siyasa ne kuma babban manomi ne a garin.

Wata majiya dake garin ta ce an kashe marigayin ne bayan da ya nuna turjiya lokacin da ƴan fashin dajin suke ƙoƙarin tafiya da shi.

Wani mutum da ya tsira daga harin ya ce ƴan bindigar sun samu nasarar yin garkuwa da mata da kuma biyu daga cikin ƴaƴan marigayin.

Mutum na biyu da aka kashe a harin wani ma’aikacin lafiya ne da yake aiki a Cibiyar Kula Da Lafiya ta Mairuwa.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]