Zan ji farin ciki idan na lashe Europa — Cech

Petr Cech

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Petre Church, golan Arsenal, ya bayyana cewa zai yi farin ciki idan har ya lashe Europa Cup a Arsenal, bayan da ya sanar zai yi ritaya a karshen kakar bana.

A watan Janairu dan wasan mai shekara 36 ya sanar zai hakura da taka-leda da an kammala wasannin 2018/19, bayan da ya ci kofuna 14 a Chelsea da Gunners.

Rashin kokarin Cech a gasar Premier ya sa Bernd Leno ya maye gurbinsa a Emirates, amma shi ne yake tsare ragar Arsenal a wasannin Europa da Caraboa.

Ana sa rana golan shi ne zai tsare ragar Arsenal a wasan da za ta ziyarci BATE Borisov a Europa League a ranar Alhamis, har ya hangi kansa a wasan karshe a gasar.

More News

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaƙi da yiwa tattalin arzikin ƙasa ne ya hana shi bayyana...