Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana gaban babbar kotun tarayya dake Abuja.

Hukumar EFCC na son ta gurfanar da Yahaya Bello ne gaban kotu inda take masa tuhume-tuhume 19 da suka shafi almundahana da kuma almubazzaranci da kuÉ—aÉ—en da suka kai naira biliyan 82.

Duk da cewa an shirya gurfanar da shi a ranar 18 ga watan Afrilu Bello ya gaza bayyana a gaban kotun.

A yayin cigaba da zaman shari’ar ranar Talata, Adeola Adedipe É—aya daga cikin lauyoyin Yahaya Bello ya ce wanda yake karewa zai iya  bayyana a gaban kotun amma yana tsoron a kama shi a tsare.

“Wanda ake Æ™ara yana so yazo kotu amma yana tsoron akwai umarnin kotu da ya bada damar a kama shi,” a cewar Adedipe.

Lauyan ya nemi kotun ta soke umarni kamun da aka bayar a ranar 17 ga watan Afrilu.

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar Æ´an sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Ƴansanda sun kama wanda ya kitsa harin da aka kai wa jirgin ƙasa a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Alhamis, ta sanar da kame wanda ake zargin ya shirya harin da aka kai a jirgin ƙasan Abuja-Kaduna...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani É“angare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...