An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air har sai sai baba ta gani.

Umarnin na zuwa ne biyo bayan hatsarin da ya rutsa da jirgin kamfanin a filin jirgin saman Murtala Muhammad dake Lagos a ranar 23 ga watan Afrilu.

Da safiyar ranar Talata ne jirgin kamfanin da ya taso daga Abuja zuwa Lagos  ya zame daga kan titinsa ya sauka Æ™asa dai-dai lokacin da yake sauka a filin jirgin saman Murtala Muhammad dake Lagos.

Hakan ya tilastawa hukumomin filin jirgin karkatar da jiragen masu sauka da tashi ya zuwa ɓangaren da jiragen dake tafiya ƙasashen waje ke sauka da tashi.

A wata wasiÆ™a mai É—auke da sahannun  babban sakataren ma’aikatar ta NCAA ,Emmanuel Meribole  ta ce an jawo hankalin ministan kan matukar damuwa da aka nuna kan lamarin.

Ma’aikatar ta ce lamarin ya jawo damuwa kan halin da kamfanin ke ciki ta fuskar kuÉ—i da kuma matakan kariya.

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar Æ´an sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Ƴansanda sun kama wanda ya kitsa harin da aka kai wa jirgin ƙasa a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Alhamis, ta sanar da kame wanda ake zargin ya shirya harin da aka kai a jirgin ƙasan Abuja-Kaduna...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani É“angare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...