Zaben 2023: Ko Tafiyar Win-Win Za Ta Iya Cin Zaben Gwamna A Kano ?

Win-Win Kano Sabuwa tafiyar ta matasa ce” wadannan sune kalaman, Engr Muazu Magaji Dansarauniya jagoran tafiyar gidan  siyasar da ake wa lakabi da Win-Win Kano Sabuwa a duk lokacin da ya karbi wasu mutane da suka kawo masa ziyara.

Engr Muazu Magaji


Burin wannan tafiya ta su bai wuce zamanantar da jihar Kano ba ta yadda birnin zai yi gogayya da sauran birane a duniya.


Duk da cewa jagoran tafiyar ya nuna sha’warsa ta gadar kujerar gwamnan Kano daga gwamna mai ci Abdullahi Umar Ganduje wasu mutane da dama suna ganin hakansa ba zai cimma ruwa ba ganin yadda akwai manyan yan takarkaru dake gabansa a jam’iyarsa ta APC.

Tinubu ko Osinbajo ina al’ummar Kano za su karkata?.
Atiku ya hadu da wasu jiga-jigan jam’iyar APC.


Biyo bayan rikicin da ya barke a jam’iyar APC inda a yanzu ake da shugabanci  tsagi biyu; shugabancin Abdullahi Abbas da gwamnatin jihar ke marawa baya da kuma na su Ahmadu Haruna Zago da yake samun goyon bayan sanata Ibrahim Shekarau, danmajalisar tarayya, Shaaban Ibrahim Sharada da sauransu.


Magaji ya zabi yin biyayya ga bangaren, Ahmadu Haruna Zago sai dai wasu na ganin cewa rara-gefe kawai yake ba shi da wani tasiri a tafiyar ta su.


“Idan ka duba zaka ga siyasa ya ke ta soki burutsu, yau ya taba wannan gobe wancan ba tare da wata alkibla guda daya ba. Duk da cewa yafi sukar gwamnati hakan baya rasa nasaba da sauke shi daga mukamin kwamishina da kuma na shugaban kwamitin aikin shimfida bututun iskar gas, “a cewar wani mai sharhi kan al’amuran yau da kullum.


Shi ma wani mai bibiyare siyasar jihar Kano ya ce “Dansarauniya ka iya zama dan hakin da ka raina a kakar zaben 2023.”
Lokaci ne kadai zai bayyana irin tasirin da tafiyar siyasar Win-Win Kano Sabuwa za ta yi a siyasar jihar Kano.

Author: Sulaiman Sa’ad
Email: info@arewa.ng

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...