Tinubu ko Osinbajo ina al’ummar Kano za su karkata? – Sulaiman Sa’ad

Tun bayan da aka shiga sabuwar shekarar 2022 wacce daga ita sai kakar babban zaben shekarar 2023 al’amura suka fara kankama kan shirye-shiryen zaben.


Lamarin dai yafi kamari a jam’iyar APC mai mulki inda yan takarkaru da dama suke ta jirwaye mai kamar wanka game da yiyuwa ko kuma akasin tsayawar su takara.

Tinubu ko Osinbajo


Kawo yanzu dai mutane biyu su aka fi an bato kan batun tsayawa takarar shugaban kasa a jamiyar APC wato tsohon gwamnan Lagos Bola Tinubu da kuma mataimakin shugaban kasa, Farfesa Yemi Osinbajo.
Da alama dai guguwar zaben na shekarar 2023 ta fara tasowa daga Kano ganin yadda wasu jiga-jigan yan siyasa daga jihar suka fara bayyana goyon bayansu ga Tinubu da kuma Osinbajo.


Tsohon danmajalisar tarayya, Abdulmumin Jibrin Kofa shi ne ya fara bayyana goyon bayansa ga Tinubu a yayin wani taron gangamin addua’a da ya shirya domin samun nasarar Tinubu a zaben na 2023.
Shima danmajalisar tarayya dake wakiltar mazabar Tarauni, Hafiz Kawu ya bayyana cewa Osinbajo ne mutumin da ya fi dacewa ya gaji shugaban kasa,Buhari.


A baya dai jama’ar Kano sun koka kan yadda ake watsi da su da zarar an samu nasarar zabe duk da irin yawan kuri’ar da suka bawa shugaban kasa, Buhari da kuma jam’iyarsa ta APC.
Abin jira a gani ko a bana za ta sauya zani. – Sulaiman Saad

More News

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...

An kori sojojin Najeriya biyu saboda satar kebul a matatar Dangote

Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da korar wasu sojoji biyu da ake zargi da satar igiyoyin sulke a harabar matatar Dangote da ke jihar...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...