Za mu sake bitar mafi karancin albashi a Najeriya—Tinubu

Shugaba Bola Tinubu ya yi alkawarin sake nazarin mafi karancin albashin ma’aikata domin dacewa da yanayin tattalin arzikin kasar nan.

A cewarsa, akwai bukatar gwamnatin tarayya da na jihohi su duba mafi karancin albashi tare da kuma karfafa tushe da aiwatar da kudaden shigar kasar.

Ya bayyana hakan ne a ranar Juma’a a lokacin da yake ganawa da ‘ya’yan kungiyar gwamnonin Progressive Governors’ Forum, wadanda suka bayyana goyon bayansu ga shugaban kasar kan cire tallafin.

Da yake magana a lokacin da ya karbi bakuncin mambobin kungiyar, Tinubu ya ce, “Muna bukatar yin wasu kididdiga da bincike kan mafi karancin albashi,” ya kara da cewa, “Dole ne mu duba hakan tare da kuma kudaden shiga. Dole ne mu karfafa tushe da kuma amfani da kudaden shigar mu.”

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...