Za mu dauki mataki kan jifar shugabanninmu a Ogun – APC

Shugaba Muhammadu Buhari

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya ta nuna rashin jin dadinta kan yadda aka jefi shugabanninta a gangamin yakin neman zaben shugaba Buhari a jihar Ogun.

Wata sanarwa da jam’iyyar ta fitar ta ce za ta dauki mataki kan gwamnan jihar Ibikunle Amosun wanda ta zarga da shirya cin mutuncin ga shugabanta Adams Oshiomhole a gaban idon shugaba Buhari.

A ranar Litinin ne wasu suka jefi Adams Oshiomhole a yayin da shugaba Muhammadu Buhari ke gangamin zabensa a birnin Abeokuta.

An jefi Oshiomhole ne bayan da ya ambaci sunan dan takarar gwamna na APC a jihar, Mista Dapo Abiodun wanda gwamnan jihar ba ya goyon baya, matakin da ya harzuka mutanen da suka halarci gangamin.

APC ta ce ba za ta lamunce wa wannan rashin da’a ba daga duk wani mambanta.

Ta ce za ta yi nazari kan abin da ya faru inda aka kunyata Buhari da shugabanninta kuma za ta dauki mataki akai bayan an kammala zabe.

Lamarin ya kai sai da jam’ian tsaro suka rika kare shugaba Buharir daga masu jifa kafin kammala taron.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...