Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar ƴan sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar.

A wata sanarwa ranar Litinin mai magana da yawun rundunar,Mansur Hassan ya ce mutanen biyu da ake zargi an kama su ne ranar 4 ga watan Afrilu biyo bayan ƙwararan bayanan sirri da aka tattara akan su.

Alkali Danladi mai shekaru 45 da kuma Gayya Koddi mai shekaru 40 su ne mutanen da aka kama.

Hassan ya ce ƴan sandan sun daɗe suna fakon  Danladi kan samarwa da ƴan fashin daji makamai inda a ƙarshe aka kama shi a ƙauyen Tsurutawa dake kan hanyar Kaduna zuwa Jos.

Ya ce an kama Danladi da makamai da dama da aka haramta amfani da su.

Ya ce faɗaɗa binciken da aka yi ne ya kai ga kama Koddi a yayin da ake cigaba da neman wasu mutane biyu.

Danladi na kan hanyarsa ta dawowa daga Jos lokacin da aka kama shi.

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Ƴansanda sun kama wanda ya kitsa harin da aka kai wa jirgin ƙasa a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Alhamis, ta sanar da kame wanda ake zargin ya shirya harin da aka kai a jirgin ƙasan Abuja-Kaduna...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani ɓangare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...