Kungiyar yan uwa musulmi ta Najeriya da aka fi sani da shi’a sun gudanar da zanga-zangar nuna goyon baya ga FalasÉ—inawa a rikicin da kungiyar Hamas take da Isra’ila.
Ranar Asabar da safe kungiyar Hamas ta kaddamar da hare-hare kan Æ™asar Isra’ila bayan da ta zarge ta da kai hari masallacin Æ™udus da kuma kan FalasÉ—inawa.
Kawo yanzu mutane da dama ne suka rasa rayukansu a dukkanin bangarorin biyu.
Tattaki na yan kungiyar ta shi’a ya fara ne da misalin Æ™arfe huÉ—u na ranar Litinin daga Bantex Plaza inda ya kare zuwa fitilar bayar da hannu dake kan titin Ahmadu Bello.