‘Yan sanda sun kama mutum 50 kan rikicin siyasa a Kano

Kano

Image caption

Makamai da hukumar ‘yan sanda ta jihar Kano ta kwace daga hannun ‘yan daba a jihar

Rundunar ‘yan sanda ta jihar Kano a Najeriya ta ce ta yi nasarar kama mutane 50 da take zargi da bangar siyasa da kwace a yayin taron siyasa da aka gudanar na PDP a jihar ranar Lahadi.

“Babu wanda ya fi karfin doka kuma duk mukaminsa sai mun hukunta shi, don doka gaba take da kowa”, in ji kwamishinan ‘yan sanda na jihar Wakili Mohammed.

“Babu yadda za a yi a ce wasu tsuraru su ji sun fi karfin doka.

“Don haka mun hana yawo da kowane irin makami, kuma mun hana fita da ‘yan banga yawon yakin neman zabe.” inji Wakili.

Har wa yau, ya kuma ce rundunar ‘yan sandan jihar za ta sanya kafar wando daya da masu sayar da kwaya da kayan maye a jihar. Wakili Mohammed ya ja hankalin iyaye da su ja kunnen ‘ya’yansu kan shiga bangar siyasa don guje wa fushin hukuma.

Yanayin siyasa a jihar Kano na kara munana duk da yarjejeniyar da yan takara suka sanya wa hannu kan yakin neman zabe da gudanar da zaben cikin lumana a jihar.

A ranar Lahadi ne ‘yan daba suka rika far wa mutane tare da yi masu kwace jim kadan bayan ziyarar da dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP Alhaji Atiku Abubakar ya kai jihar Kano domin yakin neman zabe.

Lamarin da ya jawo asarar rayuka da tare da ji wa mutane munanan raunuka.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...