Yan sanda sun harbe yan fashi biyu a Akwa Ibom – AREWA News

Rundunar yan sandan jihar Akwa Ibom ta ce ta kashe wasu yan fashi biyu a wata musayar wuta da suka yi a kauyen Ifuhe dake karamar hukumar Ikot Ekpene ta jihar.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa mai dauke da sahannun jami’in hulda da jama’a na rundunar,SP Odiko Makdon da aka rabawa manema labarai ranar Juma’a a Uyo babban birnin jihar.

A cewar mai magana da yawun rundunar, yan fashin sun hangi motar jami’an tsaro lokacin da suke tsaka da aikata ta’asa a yankin inda suka budewa motar wuta abin ya jawo aka yi musayar wuta.

Ya kara da cewa akwai yiyuwar wasu daga cikin yan fashin sun tsere cikin dajin da raunin harbin bindiga a yayin da aka tabbatar da harbe mutane biyu kuma aka tabbatar sun mutu a asibitin yan sanda dake Ikot Ekpene.

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...