Yan sanda sun harbe yan fashi biyu a Akwa Ibom – AREWA News

Rundunar yan sandan jihar Akwa Ibom ta ce ta kashe wasu yan fashi biyu a wata musayar wuta da suka yi a kauyen Ifuhe dake karamar hukumar Ikot Ekpene ta jihar.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa mai dauke da sahannun jami’in hulda da jama’a na rundunar,SP Odiko Makdon da aka rabawa manema labarai ranar Juma’a a Uyo babban birnin jihar.

A cewar mai magana da yawun rundunar, yan fashin sun hangi motar jami’an tsaro lokacin da suke tsaka da aikata ta’asa a yankin inda suka budewa motar wuta abin ya jawo aka yi musayar wuta.

Ya kara da cewa akwai yiyuwar wasu daga cikin yan fashin sun tsere cikin dajin da raunin harbin bindiga a yayin da aka tabbatar da harbe mutane biyu kuma aka tabbatar sun mutu a asibitin yan sanda dake Ikot Ekpene.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...