Sarkin Kudun Dan Sadau a jihar Zamfara ya tabbatar wa BBC cewa ‘yan fashin daji sun kashe sama da mutum 30 lokacin da suka auka wa kauyen Dan-Gurgu na masarautarsa tare da jikkata karin wasu 12.
Alhaji Hussaini Umar ya ce dukkan mutanen da abin shafa maza ne, wadanda aka far wa a lokacin da suke haramar tafiya gonakinsu wayewar garin ranar Asabar.
BBC ta tuntubi mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara, Muhammed Shehu kan wannan rahoto, sai dai bai amsa kiran waya da muka yi ta yi masa, ko musanta gajeren sakon da muka aika masa ba.
Jihar Zamfara da ke arewa maso yammacin Najeriya na fama da hare-haren ‘yan fashin daji, wadanda kan far wa kauyuka, su kashe mutane, tare da kona gidajensu har ma da dukiyar da suka mallaka. Ko da yake da farko sun fara ne da satar mutane, inda sukan rike su har sai dangi ko makusantansu sun biya kudin fansa.
Masarautar Dan Sadau da ke karamar hukumar Maru ta yi makwabtaka da yankin Birnin Gwari na jihar Kaduna, wanda ya yi kaurin suna wajen hare-haren ‘yan fashi da satar mutane.
Maharan a kan babura kimanin saba’in sun rika harbi kan mai uwa da wabi, Alhaji Hussaini Umar ya ce shi da kansa ya je asibitin Dan Sadau inda ya jajantawa mutanen da aka jikkata su goma sha biyu.
A cewar basaraken: “Likitan da ke kula da mutanen da aka jikkata ya tura biyu daga cikinsu zuwa babban asibiti saboda raunukan da aka ji musu sun tsananta.”
Ya koka game da karancin kayan aikin da jami’an tsaron da ke yankin masarautar Dan Sadau, inda ya ce: “Na yi magana da DPO lokacin da aka bugo (waya) aka hwada mana ga abin ke hwaruwa, amma al-hakikanin gaskiya, matsala bai da abin hawa kuma bai da yara mataimaka wadatattu wadanda za su iya yin hanzari (kai dauki) ga lokacin da wani abu ya hwaru.”
Alhaji Hussaini ya ce tuni mazauna kauyen Dan Gurgu suka fara tsere wa gidajensu zuwa makwabtan garuruwa da suke ganin sun fiye musu aminci.
Basaraken ya yi kira ga gwamnati da ta kai musu agaji don kuwa a cewarsa: “har yanzu mutanena suna cikin halin kaka-ni-ka-yi, manoma ba su iya zuwa don tunanin sassaben gonakinsu da shirye-shiryen gyaran ayyukan gona.”