‘Yan ciranin da suka makale sun bar wani tsibirin Italiya

stranded

Kusan ‘yan cirani 100 da ke kan wani jirgin ruwa na jin kai wanda ya makale a tsibirin Lampedusa sun bar tsibirin na Italiya, bayan wani mai shigar da kara ya umarci jirgin ruwan da ya bar tsibirin.

Lokacin da jirgin ya isa tsibirin dai, mutane sun yi musu maraba a yayin da suka dinga sowar “sannu da zuwa” musamman ma ga ‘yan ciranin Afirka.

Mai shigar da kara, Luigi Patronaggio ya umarci da a kwace jirgin wanda mallakin wata kungiyar agaji mai suna Open Arms ne.

Kungiyar ta ce ‘yan ci ranin za su iya fara samun kulawar likitoci, duk da gwamnatin Italiya ta jima tana hana su shiga kasar.

Kafin mai shigar da karar ya yanke hukuncinsa, Sipaniya wadda ita ce gida ga kungiyar ta Open Arms ta aika wani jirgin ruwa zuwa Lampedusa domin ya dauko ‘yan ci ranin.

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...