Yan Bindiga Sun Zafafa Kai Farmaki A Wasu Yankuna

Bayan da yan bindiga dadi da masu satar mutane suka dai-dai ta da dama daga cikin yankunan jihar Zamfara, wannan ta’addancin dai halin yanzu na neman samun gindin zama a jihar Katsina.

A cikin kanan hukumoni tara dake dandana kudarsu, karamar hukumar Batsari itace kan gaba inda yau kwanaki shidda ke nan jere ‘yan bingigan suke tada gari.

Malam Sani Lawal wani mazaunin Karamar hukumar da Muryar Amurka ta yi hira da shi ya bayyana cewa, ‘yan bindigar sun kai hare hare a kauyuka da dama inda suka yi kone kone suka kuma janyo asarar rayuka da kaddarori. yace sun je Kasai da Wagini suka kashe mutune sannan suka kore masu dabbobi. Bisa ga cewarshi, ‘yan bindigar sun kuma tafi garin Yar’gamji suka kashe mutane goma sha ukku, wadanda aka kai gawarwakinsu kofar gidan sarkin Batsari.

Mallam Lawal ya bayyana cewa, wadansu mutanen an kashe su ne suna gonakinsu, yayinda yace ‘yan bindigar sun tada mutanen karamar hukumar Safana baki daya, sai dai Sashen Hausa bai sami tabbacin haka daga wata majiya ba. Mallam Sani Lawal dai ya bayyana fusata da bakin cikin ganin a cewarsa, gwamnati bata daukar matakin da ya kamata na shawo kan matsalar.

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...