‘Yan bindiga sun sace wani basarake a jihar Plateau.

‘Yan bindiga sun sace wani basarake a jihar Plateau.

Basaraken Da Gyang Balak, yakasance mai fada aji a gundumar Vwang da ke karamar hukumar Jos ta Kudu.

Dan Majalisar dake wakiltar karamar hukumar a majalisar dokokin jihar ne ya tabbatarwa da jaridar Punch labarin sace basaraken.

An sace basaraken ne a ranar Lahadin data wuce da misalin karfe 8 na dare.

Rahotanni sun ce an sace shi ne a lokacin da ya ke kan hanyarsa ta komawa gida a kan titin dake yankin Kuru.

Lamarin ya faru ne kasa da wata guda bayan da wasu ‘yan bindigar suka sace wani basarake a karamar hukumar Mangu wanda daga bisani suka sake shi bayan biyan kudin fansa.

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...