Yan bindiga sun sace kwamishinan yaɗa labarai na Benue

Yan bindiga sun yi garkuwa da, Matthew Abo Kwamishinan Yada Labarai, Al’adu da Yawon Bude Ido na jihar Benue.

An yi garkuwa da Abo a gidansa dake garinsu na Zaki-Biam a karamar hukumar Ukum ta jihar ranar Lahadi da daddare.

Kwamishinan ya karbi rantsuwar kama aiki ne a matsayin mamba a majalisar zartarwar jihar a ranar 29 ga watan Agusta.

Ya fito ne daga karamar hukumar Ukum da tayi kaurin suna wajen tashin hankali.

Shedun gani da ido sun ce wasu yan bindiga ne akan babura suka sace kwamishinan daga gidansa dake Zaki-Biam kauyen da yayi fice kan kasuwan doya mafi girma a Najeriya.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]