Yan bindiga sun sace kwamishinan yaɗa labarai na Benue

Yan bindiga sun yi garkuwa da, Matthew Abo Kwamishinan Yada Labarai, Al’adu da Yawon Bude Ido na jihar Benue.

An yi garkuwa da Abo a gidansa dake garinsu na Zaki-Biam a karamar hukumar Ukum ta jihar ranar Lahadi da daddare.

Kwamishinan ya karbi rantsuwar kama aiki ne a matsayin mamba a majalisar zartarwar jihar a ranar 29 ga watan Agusta.

Ya fito ne daga karamar hukumar Ukum da tayi kaurin suna wajen tashin hankali.

Shedun gani da ido sun ce wasu yan bindiga ne akan babura suka sace kwamishinan daga gidansa dake Zaki-Biam kauyen da yayi fice kan kasuwan doya mafi girma a Najeriya.

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Ƴansanda sun kama wanda ya kitsa harin da aka kai wa jirgin ƙasa a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Alhamis, ta sanar da kame wanda ake zargin ya shirya harin da aka kai a jirgin ƙasan Abuja-Kaduna...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani ɓangare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...