Yan bindiga sun kai hari kan ofishin yan sanda a Kogi

Da tsakar daren ranar Juma’a Æ´an bindiga suka kai hari kan ofishin shiya na yan sanda dake Eika Ohizenyi a karamar hukumar Okehi ta jihar Kogi inda suka kashe wani Insifecta Jibril dake bakin aiki.

Wani mazaunin yankin, Mallam Momoh Abubakar ya bayyana cewa maharan sun mamaye ofishin yan sandan da misalin 12:15 na tsakar daren ranar Juma’a dauke da bama-bamai da sauran makamai.

Ya bayyana cewa bom na farko da suka jefa kan ofishin ya yi karar gaske da ta tashi mutane da dama daga bacci a yankin ya kara da cewa bama-baman sun lalata wani sashe na ginin ofishin.

Abubakar ya kara da cewa maharan sun ci karensu babu babbaka inda suka shafe sama da sa’o’i biyu ba tare da wani É—auki ba daga jami’an tsaro ko kuma mutanen gari.

Ya bayyana cewa jami’in dan sanda É—aya tilo dake bakin aiki, Jibril wanda aka fi sani da Yellow an kashe shi a harin yayin da aka lalata motar sintiri É—aya da ofishin yake da ita.

Yan bindigar sun lalata tagogin babban masallacin Eika da kuma na cocin Katolika dake garin.

Tuni kwamishinan yan sandan jihar, Edward Egbuka ya bada umarnin tura karin jami’an tsaro zuwa yankin.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...