‘Yan bindiga sun kai hari a jihar Jigawa

Getty Images

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a jihar Jigawa ta tabbatar cewa barayi sun halaka mutum daya tare da jikkata wasu mutane, a wani hari da barayin suka kai a garin Maidawa da ke jihar.

Bayanai sun ce maharan sun shiga kauyen ne kan babura, sannan suka je gidan wani attajiri a kauyen suka karbi kudi, suka kuma harbe shi tare da wasu mutanen garin.

Cikin wandanda aka harba har da wasu yara uku kamar yadda aka bayyana.

Duk da cewa ‘yan sanda sun bayyana cewa mutum daya aka kashe, amma mazauna garin na ikirarin kashe mutane da dama a harin da barayin suka kai.

An bayyana cewa barayin sun kai kusan mintuna arba’in suna cin karensu ba babbaka a cikin garin na Maidawa.

Mazauna kauyen sun koka bisa ga faruwar wannan lamarin inda suke ganin kamar irin abubuwan da ke faruwa a wasu wurare sun fara isowa yankin su.

Wasu kuma mazauna garin sun shaida cewa da wayansu ba su taba ganin an kawo hari da bindigogi ba a garin.

Wannan harin da aka kai a Jigawa na zuwa ne a daidai lokacin da matsalar garkuwa da mutane da kuma fashi da makami ke kara kamari musamman a jihohin arewa maso yammacin Najeriya.

Sai dai gwamnatin kasar ta bayyana cewa tana iya bakin kokarinta wajen shawo kan matsalolin.

More News

CBN ya dakatar da kudirinsa na sa bankuna su riƙa cajar kwastomominsu

Babban bankin Najeriya ya umarci bankunan da su dakatar da cajin kudaden ajiya har zuwa ranar 30 ga Satumba, 2024.Babban bankin ya bayyana hakan...

Ƴansanda sun kama likitan bogi

Rundunar ‘yan sanda ta Zone 2, Onikan, Legas, ta kama wani likitan jabu mai shekaru 37, kuma ma’aikacin lafiya, tare da zargin amfani da...

Gwamnan Kano ya sanya hannu kan dokar yin gwajin lafiya kafin aure

Gwamnan jihar Kano, Engr Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan wata doka za ta tilastawa masu yin aure yin wasu gwaje-gwajen lafiya gabanin...

Ƴan sanda sun kama masu garkuwa da mutane da suka yi bacci a lokacin da suke tsare da mutanen da suka sace

Jami'an Æ´an sanda sun samu nasarar kama wasu masu garkuwa da mutane bayan da suka buge da sharar bacci a lokacin da suke tsare...