CBN ya dakatar da kudirinsa na sa bankuna su riƙa cajar kwastomominsu

Babban bankin Najeriya ya umarci bankunan da su dakatar da cajin kudaden ajiya har zuwa ranar 30 ga Satumba, 2024.

Babban bankin ya bayyana hakan ne a wata takarda mai dauke da kwanan watan Mayu 6, 2024, mai dauke da sa hannun Daraktan sa ido kan harkokin bankuna, Adetona Adedeji.

Abokan ciniki na wasu Bankunan sun nuna damuwarsu kan yadda bankunan suka fara tattara kudaden  ajiya na tsabar kudi tun daga ranar 1 ga Mayu.

Manema labarai sun ga haka ne a wani sakon imel da daya daga cikin kwastomomin bankin ya tura.

Dangane da matakin da bankin ya dauka, kashi biyu cikin 100 na kudaden ajiya sama da N500,000 za a cire ga daidaikun mutane, yayin da masu rike da asusu na kamfanoni kuma za a caje su kashi biyu bisa dari akan ajiya sama da N3m.

More News

Najeriya za ta dena shigo da man fetur a cikin watan Yuni – Dangote

Aliko Dangote mutumin da ya fi kowa arziki a Nahiyar Afirka ya ce Najeriya za ta daina shigo da man fetur a cikin watan...

An ceto mutane 9 daga wani ginin bene da ya ruguzo a jihar Niger

Mutane 9 aka samu nasarar cetowa daga wani ginin bene mai hawa ɗaya da ya ruguzo a yankin Sabon Gwari dake garin Minna babban...

An yi faɗa tsakanin masu sayar da waya da sojoji a kasuwar Abuja

Rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya, ta tura jami’an leken asiri zuwa kasuwar Banex – wata kasuwar kayan lantarki da na’urorin sadarwa da ke...

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...