Yan bindiga sun kai farmaki kan motocin maniyata aikin hajji a Sokoto

Yan bindiga sun buÉ—e wuta kan ayarin motacin alhazai a ranar Litinin a Sokoto.

Lamarin ya faru ne a ranar Litinin lokacin da ake kai maniyyatan filin jirgi domin su tashi zuwa kasa mai tsarki a ranar Talata.

Wasu majiyoyi sun bayyana cewa wasu daga cikin Ć´an bindigar sun samu raunuka lokacin da suke musayar wuta da jami’an tsaron da ake bawa ayarin motocin kariya.

Yan bindigar sun yi wa mahajjatan kwanton bauna a wajen dajin Gundumi amma jami’an tsaro sun samu nasarar dakile hari.

Babban sakataren din-din a hukumar alhazai ta jihar Sokoto,Shehu Dange ya tabbatar da faruwar lamarin.

“Muna san mu san halin da maniyyatan suke ciki. An ceto su duka? Ko kuma akwai wani daga cikin su da ya jikkata,” ya ce.

More News

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miĆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaĆ™i da yiwa tattalin arzikin Ć™asa ne ya hana shi bayyana...