Ya kamata a ɗauki mataki a kan Rasha, inji Shugaban Amurka Biden

Shugaban Amurka Joe Biden, ya yi kira ga kasashen Majalisar Dinkin Duniya da su tashi tsaye don yakar abin da ya kira laifukan yaki daga Rasha.

A cewarsa, tabbatar da ‘yancin cin gashin kan kowace kasa da kuma kare hakkin bil’adama shi ne babban abin da ke cikin daftarin Majalisar Dinkin Duniya.

Joe Biden na magana ne a wani bangare na taron Majalisar Dinkin Duniya na shekara-shekara a birnin New York.

A shekara ta biyu a jere ya ce wannan taro ya yi duhu da inuwar wannan yaki da Rasha ta haifar ba tare da tsayawa ba.

“Rasha ta yi imanin cewa duniya za ta nuna gajiyawa, kuma duniya za ta bar Rasha ta zalunci Ukraine, ba tare da jin kai ba.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]