Yaƙin Sudan: Za a yi tattaunawa tsakanin bangarorin da ke rikici

Ana ganin rikicin da ake yi a kasar Sudan zai zo karshe yayin da bangarorin da suke fada suka hallara a kasar Saudiyya domin gudanar da tattaunawar zaman lafiya a karon farko tun bayan barkewar yakin a tsakiyar watan Afrilu.

Za a yi tattaunawar ne bayan Saudiyya da Amurka sun dauki nauyinta.

Yarjejeniyar tsagaita bude wuta da dama a baya sun ci tura tun farkon yakin makonnin da suka gabata.

In ba a manta dai wannan yaƙi ya shafi mutane da yawa, ciki har da ƴan Najeriya da ke karatu a ƙasar ta Sudan.

Hakan ya tilasta wa gwamnatin Najeriya kwaso ɗaukacin ƴan kasar da ke can bayan an samu matsaloli da dama a wannan yunkurin.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]