Wani likitan bogi ya shiga hannun ‘yan sanda

Rafiu Ibrahim likitan bogi dake gudanar da wani haramtaccen asibiti ya fada hannun jami’an yan sanda dake aiki a sashen binciken manyan laifuka na rundunar yansanda shiya ta 11 dake Osogbo.

Mutumin da ake zargi wanda ke da shedar takardar kammala sakandare ya shafe lokacin mai tsawo yana gudanar da asibitin a wani gidan kasa mai daki daya inda yake duba marasa lafiya dake da cutuka daban-daban.

Bayanan sirri sun nuna cewa likitan bogin ya dade yana kwantar da marasa lafiya tare da zubar da ciki da kuma maganin cututtuka da suke da wuyar sha’ani inda yin hakan ke jefa rayuwar mutane cikin hatsari.

Mutumin da ake zargin ya amince da aikata laifin amma ya dora alhakin haka kan rashin aikin yi.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...