Wani jami’in kwastam ya harbe kansa har lahira a Kano

Wani jami’in hukumar kwastam ya harbe kansa har lahira a gidansa dake unguwar Farm Centre a cikin birnin Kano.

Mai magana da yawun rundunar Æ´an sandan jihar, Abdullahi Haruna Kiyawa shi ne ya tabbatar da faruwar lamarin cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Litinin.

Kiyawa ya ce jami’in mai suna Abdullahi Magaji na aiki ne a hedkwatar hukumar ta kwastam dake Abuja ana zargin cewa ya kashe kansa ne a ranar 06 ga watan Mayu.

Babban baturen Æ´an sanda na Farm Centre shi ne ya jagoranci jami’an Æ´an sanda ya zuwa gidan da abun ya faru.

Tuni dai kwamishinan Æ´an sandan jihar, Mohammed Usaini Gumel ya bayar da umarnin gudanar da cikakken bincike kan lamarin.

More News

Zanga-zanga: An jibge Æ´an sanda 4200 a Abuja

Rundunar Æ´an sandan birnin tarayya Abuja ta tura Æ´an sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haÆ™uri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...