Wani Dattijo Ya Rataye Kansa Har Lahira

Wani dattijo mai shekaru 80 mai suna Isiyaka Ayinde ya kashe kansa a Watch Tower da ke unguwar Araromi Imota a jihar Legas.

Rahotanni sun nuna cewa lamarin ya faru ne da misalin karfe 7:30 na dare a ranar Alhamis.

Majiyar ‘yan sanda ta shaida wa manema labarai cewa, marigayin ya rataye kansa da igiya a cikin kicin.

“Ya ji ’ya’yansa suna ta ihu cewa ya zo ya ga Baba a kicin. Da gudu ya shiga cikin kicin ɗin, sai ya tarar da gawar dan hayar a rataye a jikin wata igiya,” inji majiyar ‘yan sandan.

Da aka tuntubi jami’in hulda da jama’a na ‘yan sandan jihar.  , Benjamin Hundeyin, ya tabbatar da faruwar lamarin.

More News

An kama mutane biyu  masu garkuwa da mutane a jihar Kogi

Wasu ɓatagari biyu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne jami'an ƴan sanda da haɗin gwiwar ƴan bijilante suka kama a garin Ibobo-Abocho...

Jirgi mai saukar ungulu ya yi hatsari a Akwa Ibom

Wasu ma'aikatan kamfanin haƙar man fetur su 6 da kuma matuƙan jirgi su biyu su mutu a wani hatsarin jirgi mai saukar ungulu a...

Tinibu ya aikawa da majalisar dattawa sunaye 7 na  ministocin da zai naɗa

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya yi kira ga majalisar dattawa da ta tabbatar da sunayen mutane 7 da ya tura majalisar da zai...

Gwamnatin Abia za ta fara biyan albashi mafi maranci na naira 70,000 a watan Oktoba

Gwamnatin Jihar Abia ta sanar da cewa za ta fara biyan sabon albashi mafi karanci na naira 70,000 ga ma’aikatanta daga watan Oktoba 2024.Kwamishinan...