Wadanda Suka Kamu Da COVID-19 a Afirka Sun Haura 500,000

Hukumar lafiya ta duniya ta ce adadin wadanda suka kamu da cutar COVID-19 a nahiyar Afirka ya haura dubu 500,000, kuma akwai damuwa yayin da karin kasashe ke fuskantar karuwar masu kamuwa da cutar.

Sanarwar da hukumar ta WHO ta fidda ta ce ya zuwa yanzu, cikin kasa da wata biyar, cutar COVID-19 ta lakume rayuka 11,959, abinda ya haura rayuka 11,308 da aka rasa sakamakon barkewar cutar Ebola mai muni a yankin Afirka ta Yamma tsakamin shekarar 2014 zuwa 2016.

Adadin wadanda suka kamu da cutar ya linka sosai a kasashe 22 na yankin a cikin watan da ya gabata. Kusan kashi biyu cikin uku na kasashen na fuskantar yaduwar cutar a tsakanin al’umma.

Kasashen Algeria, Masar, Ghana, Najeriya da kuma Afirka ta Kudu suna da kusan kashi 71 cikin 100 na wadanda suka kamu da cutar a nahiyar. Afirka ta Kudu kadai na da kashi 43 cikin 100.

Yayin da cutar COVID-19 ke cigaba da yaduwa, dubban ma’aikatan lafiya sun kamu da rashin lafiya. Samar da kayayyaki da kare ma’aikatan lafiya shine muhimin abu a yaki da annobar COVID-19.

Hukumar WHO na aiki don tallafa wa kasashen da ke yaki da annobar COVID-19 ta hanyar samar da bayanai kan abinda ya kamata su yi, da muhimman kayayyakin aiki, kuma hukumar ta horar da ma’aikatan lafiya sama da dubu 25 daga nesa.

More News

Zanga-zanga: An jibge Æ´an sanda 4200 a Abuja

Rundunar Æ´an sandan birnin tarayya Abuja ta tura Æ´an sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haÆ™uri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...