Wadanda ke kan gaba a cin kwalle a manyan gasar Turai

Weekly football

Asalin hoton, Getty Images

A karshen makon nan za a ci gaba da gasar kasashen Turai, bayan buga fafatawar neman gurbin shiga gasar cin kofin duniya.

Tuni tawagar Jamus ta zama ta farko da ta samu gurbin shiga gasar duniya da za a yi a Qatar a 2022, bayan da ta doke Arewacin Macedonia 4-0 ranar Litinin.

Jamus din ta samu wannan damar duk da saura wasa biyu ya rage mata a karawar cikin rukuni.

Yanzu kyma hankali zai koma wasannin gasar cin kofin kasashen Turai musamma Premier League da La Liga da Serie A da Bundesliga da kuma Ligue 1.

Za a ci gaba da wasannin mako na takwas a gasar Premier League, wadda kawo yanzu aka buga karawa 70 aka kuma ci kwallo 184, bayan kammala fafatawar mako na bakwai.

Asalin hoton, Getty Images

Jarmie Vardy na Leiceter City ya ci kwallo shida daga tara da kungiyar ta zura a raga a bana kawo yanzu.

Dan wasan Liverpool, Mohamed Salah, shima shida ya ci daga 17 da kungiyar ta zura a raga.

Ga jerin wadanda ke kan gaba a cin kwallaye a gasar Premier League:

  • Jamie Vardy Leicester City 6
  • Mohamed Salah 6
  • Michail Antonio West Ham United 5
  • Neal Maupay Brighton & Hove Albion 4
  • Ismaila Sarr Watford 4
  • Bruno Fernandes Manchester United 4
  • Sadio Mane Liverpool 4

Wasanin mako na takwas da za a kara a Premier League:

Ranar Asabar 17 ga watan Oktoba

  • Watford da Liverpool
  • Aston Villa da Wolverhampton Wanderers
  • Manchester City da Burnley
  • Southampton da Leeds United
  • Leicester City da Manchester United
  • Norwich City da Brighton & Hove Albion
  • Brentford da Chelsea

Ranar Lahadi 17 ga watan Oktoba

  • Everton da West Ham United
  • Newcastle United da Tottenham

Ranar Litinin 18 ga watan Oktoba

  • Arsenal da Crystal Palace

A gasar La Liga ta Sifaniya kuwa an buga karawar mako na takwas da jumulla aka fafata sau 77 da cin kwallo 141, inda Karim Benzema na Real Madrid ke kn gaba da kwallo tara a raga.

Asalin hoton, Getty Images

Wadanda ke kan gaba a cin kwallaye a gasar La Liga:

  • Karim Benzema Real Madrid 9
  • Mikel Oyarzabal Real Sociedad 6
  • Vinicius Junior Real Madrid 5
  • Arnaut Danjuma Groeneveld Villarreal 4
  • Luis Suarez Atletico Madrid 4
  • Willian Jose Real Betis 4

Wasannin mako na tara da za a buga a La Liga:

Ranar Asabar 16 ga watan Oktoba

  • Levante da Getafe
  • Real Sociedad da Real Mallorca

Ranar Lahadi 17 ga watan Oktoba

  • Rayo Vallecano da Elche
  • Celta de Vigo da Sevilla
  • Villarreal da Osasuna
  • Real Madrid da Athletic Bilbao
  • Granada da Atletico Madrid
  • Barcelona da Valencia

Ranar Litinin 18 ga watan Oktoba

  • Deportivo Alaves da Real Betis
  • Espanyol da Cadiz

Ita kuwa gasae Serie A ta Italiya an buga karawa 70 da cin kwalo 224, inda Edin Džeko da kuma Ciro Immobile kowanne ya ci shida-shida a raga.

Asalin hoton, Getty Images

Wadanda ke kan gaba a cin kwallae a Serie A:

  • Edin Dzeko Inter Milan 6
  • Ciro Immobile Lazio 6
  • Lautaro MartinezInter Milano 5
  • Mattia Destro Genoa 4
  • Victor Osimhen Napoli 4
  • Joao Pedro Galvao Cagliari 4
  • Dusan Vlahovic Fiorentina 4
  • Lorenzo Pellegrini Roma 4
  • Jordan Veretout Roma 4

Wasannin mako na takwas da za a buga a gasar Italiya:

Ranar Asabar 16 ga watan Oktoba

  • Spezia da Salernitana
  • Lazio da Inter Milan
  • AC Milan da Hellas Verona

Ranar Lahadi 17 ga watan Oktoba

  • Cagliari da Sampdoria
  • Empoli da Atalanta
  • Udinese da Bologna
  • Genoa da Sassuolo
  • Napoli da Torino
  • Juventus da Roma

Ranar Litinin 18 ga watan Oktoba

(BBC Hausa)

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...