
Asalin hoton, Getty Images
A karshen makon nan za a ci gaba da gasar kasashen Turai, bayan buga fafatawar neman gurbin shiga gasar cin kofin duniya.
Tuni tawagar Jamus ta zama ta farko da ta samu gurbin shiga gasar duniya da za a yi a Qatar a 2022, bayan da ta doke Arewacin Macedonia 4-0 ranar Litinin.
Jamus din ta samu wannan damar duk da saura wasa biyu ya rage mata a karawar cikin rukuni.
Yanzu kyma hankali zai koma wasannin gasar cin kofin kasashen Turai musamma Premier League da La Liga da Serie A da Bundesliga da kuma Ligue 1.
Za a ci gaba da wasannin mako na takwas a gasar Premier League, wadda kawo yanzu aka buga karawa 70 aka kuma ci kwallo 184, bayan kammala fafatawar mako na bakwai.
Asalin hoton, Getty Images
Jarmie Vardy na Leiceter City ya ci kwallo shida daga tara da kungiyar ta zura a raga a bana kawo yanzu.
Dan wasan Liverpool, Mohamed Salah, shima shida ya ci daga 17 da kungiyar ta zura a raga.
Ga jerin wadanda ke kan gaba a cin kwallaye a gasar Premier League:
Wasanin mako na takwas da za a kara a Premier League:
Ranar Asabar 17 ga watan Oktoba
Ranar Lahadi 17 ga watan Oktoba
Ranar Litinin 18 ga watan Oktoba
A gasar La Liga ta Sifaniya kuwa an buga karawar mako na takwas da jumulla aka fafata sau 77 da cin kwallo 141, inda Karim Benzema na Real Madrid ke kn gaba da kwallo tara a raga.
Asalin hoton, Getty Images
Wadanda ke kan gaba a cin kwallaye a gasar La Liga:
Wasannin mako na tara da za a buga a La Liga:
Ranar Asabar 16 ga watan Oktoba
Ranar Lahadi 17 ga watan Oktoba
Ranar Litinin 18 ga watan Oktoba
Ita kuwa gasae Serie A ta Italiya an buga karawa 70 da cin kwalo 224, inda Edin Džeko da kuma Ciro Immobile kowanne ya ci shida-shida a raga.
Asalin hoton, Getty Images
Wadanda ke kan gaba a cin kwallae a Serie A:
Wasannin mako na takwas da za a buga a gasar Italiya:
Ranar Asabar 16 ga watan Oktoba
Ranar Lahadi 17 ga watan Oktoba
Ranar Litinin 18 ga watan Oktoba
(BBC Hausa)