Usman Bugaje: Yadda dan siyasar ya gamu da fushin DSS saboda caccakar Buhari

Usman Bugaje

Asalin hoton, OTHER

Masu amfani da shafukan sada zumunta a Najeriya musamman shafin Twitter sun fusata sakamakon matakin da hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta dauka na gayyatar Dr Usman Bugaje saboda ya soki gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari.

Dr Bugaje, wanda ya yi hira da gidan talbijin na AIT a makon nan, ya caccaki gwamnatin Buhari bisa gazawarta wajen tabbatar da tsaro a kasar musamman a Arewa.

Ya yi kira ga shugaban kasar da ‘yan majalisun dokokin tarayya su sauka daga mukamansu idan ba za su iya tabbatar da tsaro a kasar ba.

“Idan ba za ku iya gyara matsalolin kasar nan ba, ya kamata ku sauka daga mulki. Me kuke yi a kan mukamanku? Su ma ‘yan majalisar dokoki, suna zaune suna jin dadin albashi da sauran alawus-alawus yayin da kasar nan take rugujewa kuma babu abin da suke yi. Wannan kasar tana rugujewa amma kuna nan a zaune kuna ta bayar da uzuri,” in ji Dr Bugaje.

Wadannan kalamai sun jawo masa gayyata daga hukumar DSS inda wasu rahotanni suka ce ya kwashe tsawon wunin Laraba yana amsa tambayoyi.

Masu lura da lamura da sharhi kan ci gaban Najeriya irin su Dr Mairo Mandara sun kwashe tsawon ranar suna jiran ganin an saki dan siyasar, wanda da shi aka kafa jam’iyyar APC mai mulkin kasar.

Ba wannan ne karon farko da fitaccen masanin yake sukar gwamnatin Shugaba Buhari ba saboda abin da ya kira gazawarta wajen tabbatar da tsaro a kasar.

Dr Bugaje, wanda dan asalin jihar Katsina ne da ke fama da hare-haren ‘yan fashin daji da masu garkuwa da mutane, ya taba samun gayyata daga wurin Shugaba Buhari domin ya zama jakadan Najeriya a wata kasa amma ya ki karba yana mai cewa ci gaban arewacin Najeriya ne babban abin da zai sanya a gaba.

Me ‘yan Twitter suke cewa?

Asalin hoton, NIGERIA PRESIDENCY

Bayanan hoto,
Dr Usman Bugaje ya yi kira ga Shugaba Buhari ya sauka daga mulki idan ba zai iya kare rayukan jama’a ba

Gayyatar da DSS ta yi wa dan siyasar ta haifar da suka daga masu amfani da Twitter inda sunan Usman Bugaje ya kasance daya daga cikin manyan batutuwan da aka fi tattaunawa a shafin.

Da yake tsokaci kan batun, fitaccen mai sharhin nan kan harkokin yau da kullum, Farfesa Jibrin Ibrahim ya ce “gwamnatin [Buhari] tana yi wa kanta babbar illa saboda yadda take tsare da kuma musgunawa masu sukarta. Mun dade muna yaki domin tabbatar da ‘yancin jama’a kuma babu wanda ya isa ya rufe mana baki.”

Ita kuwa kungiyar kare hakkin dan adam ta Amnesty International jan hankali ta yi game da labarin gayyatar da DSS ta yi wa Usman Bugaje.

A nata bangaren, ‘yar Kafanchan, ta koka kan yadda mutane suke yin shiru yayin da Buhari yake “hukunta ‘yan arewa da suka soki” gwamnatinsa tana mai cewa a bara ma sai da jami’an tsaro suka tsangwami matarsa saboda ta bayyana ra’ayinta kan matsalolin da kasar take ciki.

(BBC Hausa)

More News

Yadda rikici a kan gishirin N20 ya yi sanadiyyar mutuwar wani mutum a Kano

Wani magidanci mai suna Zakari Hamza mai shekaru 45, ya gamu da ajalinsa a hannun kanen matarsa, wani Magaji Salisu saboda gishirin N20. Dan marigayin,...

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan IPOB 5

Dakarun rundunar sojan Najeriya da kuma ta rundunar sojan ruwan Najeriya a ranar Talata sun kashe mayaƙan ƙungiyar IPOB guda biyar a yayin musayar...

ĆŠan agajin Izala ya samu lambar yabo, kujerar hajji, kyautar mota bayan ya tsinci naira miliyan 100 ya mayar wa mai su

Salihu AbdulHadi Kankia, mamba ne na kungiyar agaji ta kungiyar Jama’atu Izalatil Bid’ah Wa Iqamatus Sunnah (JIBWIS), ya samu yabo da tukuicin mayar da...

Musulmi a Zaria sun yi taron addu’o’i saboda mummunan halin matsi da Najeriya ke ciki

Musulmi a garin Zaria na jihar Kaduna, sun gudanar da addu'a ta musamman domin neman taimakon Allah kan halin da 'yan Najeriya ke ciki...