Twitter zai dawo aiki a Najeriya bayan haramta shi na tsawon kwana sama da 200

Gwamnatin Najeriya ta kawo ƙarshen hanin da ta yi wa ƴan ƙasarta game da amfani da kafar sadarwa ta Twitter.

Wannan na zuwa ne bayan shafe sama da kwanaki 200 ba tare da yin Twitter ba, sai dai ta haramtacciyar hanya.

Shugaba Buhari ya amince da kawo ƙarshen haramcin ne bayan bangaren gwamnatin da na Twitter ɗin sun cim ma matsaya.

Ministan Sadarwa, Dr. Isah Ali Pantami, shi ne ya rubuta w shugaba Buhari cikin wata wasika cewa za a iya dawo da kafar.

More News

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...

Yadda rikici a kan gishirin N20 ya yi sanadiyyar mutuwar wani mutum a Kano

Wani magidanci mai suna Zakari Hamza mai shekaru 45, ya gamu da ajalinsa a hannun kanen matarsa, wani Magaji Salisu saboda gishirin N20. Dan marigayin,...

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan IPOB 5

Dakarun rundunar sojan Najeriya da kuma ta rundunar sojan ruwan Najeriya a ranar Talata sun kashe mayaƙan ƙungiyar IPOB guda biyar a yayin musayar...