Tsokacin masana game da kalaman Buhari a taron ministoci

Fadar shugaban Najeriya ta shirya taron sanin makamar aiki ga sabbin ministoci da shugaban ya nada domin gudanar da gwamnati a zango na biyu.

Yanzu haka masu fashin baki a fannin siyasar Najeriya na tsokaci game da kalaman da shugaban kasar ya yi a lokacin da ya gabatar da jawabi a wurin taron sanin makamar aikin ga asabbin ministocin da ya nada.

Batutuwan da shugaban na Najeriya ya tabo, a wurin taron, sun hada da bitar nasarorin zangon farko na gwamnatinsa da kalubalen yawan jama’a da Najeriya ke fuskanta da mafarkin gwamnatinsa na aza tubalin fitar da matalauta miliyan 100 daga kangin fatara cikin shekaru 10 masu zuwa.

Shugaban ya kuma tabo batun bukatar da ke akwai ga sabbin ministocin su hada hannu wuri guda ta fuskar tsarawa da aiwatar da manufofin cimma burin gwamnati a ma’aikatun da za su jagoranta.

Sai dai masu kula da lamura sun yi tsokaci game da lafuzzan shugaban.

Kwamared Kabiru Sa’idu Dakata, shugaban kungiyar CAJA masu rajin tabbatar da adalci kawar da rashawa da kuma alkinta dukiyar kasa, ya ce bayannan shugaban sun saka shakku a zukatan jama’ar kasar.

Ya kuma kara da cewa jawabin nasa ya nuna cewa ita gwamnati ba ta da shirin da za ta kai kasar ga inda ta ce za ta kai ta.

Shi ma masanin kimiyyar siyasa da harkokin dimokaradiya, ya yi tafsili game da kalaman na shugaba Buhari.

Malam Kabiru Sufi, malami ne a kwalejin share fagen shiga Jami’a ta Kano, ya kuma ce jama’a suna jiran su ga an fitar da wani daftari ko wani babban kudiri da ya wuce wanda aka fitar a halin yanzu.

Yanzu dai ‘yan Najeriya na dakon ganin kamun ludayin sabbin ministocin bayan shugaba Buhari ya tura su ma’aikatun da za su yi wani lokaci a nan gaba.

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...