Tsohon gwamna Shema ya ziyarci gwamna Dikko Radda

Tsohon gwamnan jihar Katsina, Ibrahim Shehu Shema ya ziyarci gwamna mai ci, Dikko Radda a gidan gwamnatin jihar.

Shema wanda ya mulki jihar Katsina daga shekarar 2007 zuwa 2015 a karkashin jam’iyar PDP ya kai ziyarar ne tare da yan tawagarsa.

A wata sanarwa da mataimaki na musamman ga gwammnan jihar kan kafafen sadarwar zamani, Isah Miqdad ya fitar ya ce tsohon gwamnan ya ce ya kai ziyarar ne domin taya gwamna Radda murna kan yadda aka rantsar da shi lafiya.

Shema ya ce jihar Katsina na bukatar mutane irin Radda domin kawo cigaba ya kuma yaba da kokarinsa na dawo da jihar turbar cigaba kamar yadda take a baya.

A nasa jawabin gwamna Radda ya godewa tsohon gwamnan kan ziyarar da kuma yi masa murna kan gudunmawar da ya bayar wajen samun nasarar yin zaben da aka yi lafiya.

More News

An samu ambaliyar ruwa a Adamawa

Anguwan Tana, al’ummar karamar hukumar Yola ta Arewa, sun shiga tasgaro a ranar Alhamis sakamakon ambaliya daga kogin Kilange da kogin Faro. Mazaunan garin...

Sojoji sun ceto mutane 6 daga cikin É—aliban jami’ar Gusau da aka sace

Sojoji sun ceto dalibai mata shida daga cikin daliban Jami'ar Gwamnatin Tarayya dake Gusau da aka bada rahoton yan bindiga sun yi garkuwa da...

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da É—aliban Jami’ar Tarayya da ke Gusau

An sace wasu daliban jami’ar tarayya ta Gusau da ba a tantance adadinsu ba da sanyin safiyar Juma’a. ‘Yan ta’addan masu yawan gaske sun...

Yan sanda sun gano haramtacciyar masana’antar Æ™era makamai Cross River

Rundunar yan sandan jihar Rivers ta ce ta bankaɗo wata haramtacciyar masana'antar ƙera bindigogi da nakiyoyi dake garin Osomba a karamar hukumar Akamkpa ta...