Tsohon gwamna Shema ya ziyarci gwamna Dikko Radda

Tsohon gwamnan jihar Katsina, Ibrahim Shehu Shema ya ziyarci gwamna mai ci, Dikko Radda a gidan gwamnatin jihar.

Shema wanda ya mulki jihar Katsina daga shekarar 2007 zuwa 2015 a karkashin jam’iyar PDP ya kai ziyarar ne tare da yan tawagarsa.

A wata sanarwa da mataimaki na musamman ga gwammnan jihar kan kafafen sadarwar zamani, Isah Miqdad ya fitar ya ce tsohon gwamnan ya ce ya kai ziyarar ne domin taya gwamna Radda murna kan yadda aka rantsar da shi lafiya.

Shema ya ce jihar Katsina na bukatar mutane irin Radda domin kawo cigaba ya kuma yaba da kokarinsa na dawo da jihar turbar cigaba kamar yadda take a baya.

A nasa jawabin gwamna Radda ya godewa tsohon gwamnan kan ziyarar da kuma yi masa murna kan gudunmawar da ya bayar wajen samun nasarar yin zaben da aka yi lafiya.

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...