Tsohon firaministan Birtaniya Tony Blair ya ziyarci Tinubu

Tony Blair, tsohon Firayim Ministan Burtaniya, ya ziyarci Asiwaju Bola Tinubu, shugaban kasa mai jiran gado, a ranar Talata.

Wannan dai na zuwa ne mako guda kafin rantsar da zababben shugaban kasar.

Wata majiya ta kusa da zababben shugaban kasar ta tabbatar da ziyarar ta Blair, inda ta kara da cewa ya kai ziyarar ne domin tattaunawa da Mista Tinubu.

Ya ce, “Bani da cikakken bayani tukuna. Amma na yi imanin hakan na da nasaba da kulla alaka tsakanin Najeriya da Birtaniya. Ina fata kuna sane da cewa Sakataren Amurka ma ya kira Asiwaju a makon jiya.”

Shugaban majalisar wakilai Femi Gbajabiamila da mataimakin shugaban kasa mai jiran gado Kashim Shettima sun halarci taron.

More News

An Jikkata Jami’an Tsaro A Harin Da Ƴan Bindiga Su ka Kai Wa Ayarin Motocin Yahaya Bello

A jikkata wasu jami'an tsaro a wani hari da yan bindiga su ka kai kan jerin ayarin motocin gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ranar...

Bala Muhammad ya zama shugaban gwamnonin jam’iyyar PDP

An zaɓi gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad a matsayin sabon shugaban kungiyar gwamnonin jam'iyyar PDP. Siminalayi Fabura zaɓaɓɓen gwamnan jihar Rivers shi ne mataimakin shugaban...

Za mu sake bitar mafi karancin albashi a Najeriya—Tinubu

Shugaba Bola Tinubu ya yi alkawarin sake nazarin mafi karancin albashin ma’aikata domin dacewa da yanayin tattalin arzikin kasar nan. A cewarsa, akwai bukatar...

EFCC na zargin tsohuwar ministar mata a mulkin Buhari da karkatar da naira biliyan 2

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin kasa ta'annati ta titsiye tsohuwar ministar harkokin mata Pauline Tallen kan zargin azurta kai ta...