Tsohon firaministan Birtaniya Tony Blair ya ziyarci Tinubu

Tony Blair, tsohon Firayim Ministan Burtaniya, ya ziyarci Asiwaju Bola Tinubu, shugaban kasa mai jiran gado, a ranar Talata.

Wannan dai na zuwa ne mako guda kafin rantsar da zababben shugaban kasar.

Wata majiya ta kusa da zababben shugaban kasar ta tabbatar da ziyarar ta Blair, inda ta kara da cewa ya kai ziyarar ne domin tattaunawa da Mista Tinubu.

Ya ce, “Bani da cikakken bayani tukuna. Amma na yi imanin hakan na da nasaba da kulla alaka tsakanin Najeriya da Birtaniya. Ina fata kuna sane da cewa Sakataren Amurka ma ya kira Asiwaju a makon jiya.”

Shugaban majalisar wakilai Femi Gbajabiamila da mataimakin shugaban kasa mai jiran gado Kashim Shettima sun halarci taron.

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...