Tottenham ta ci gaba da bude wuta a Firimiya

Tottenham

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Tottenham ta casa Leicester City da ci 3-1 a wasan mako na 26 a gasar cin kofin Premier da suka fafata a ranar Lahadi a Wembley.

Tottenham ta fara cin kwallo ta hannun Davinson Sanchez a minti na 33 da fara wasa, Leicester ta samu damar farkewa a bugun fenariti, amma Jamier Vardy ya barar.

Bayan da aka koma daga hutu ne Eriksen ya kara na biyu daga baya Vardy na Leicester ya zare daya, sai dai daf da za a tashi daga fafatawar Son Heung-Mi ya ci na uku.

Da wannan sakamakon Tottenham tana nan a mataki na uku da maki 60, maki biyar tsakaninta da Liverpool ta daya a teburi, sannan maki biyu tsakaninta da City wadda za ta karbi bakuncin Chelsea.

A ranar Asabar Liverpool ta doke Bournemouth da ci 3-0 a karawar mako na 26 a gasar ta Premier da suka kara a Anfield.

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...