Tinubu ya miƙa tuta ga ƴan takarar APC a zaɓukan gwamna na jihohin Kogi, Bayelsa da Imo

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya miƙa tuta ga yan takarar gwamna a jam’iyar APC a zaɓen da za ayi a jihohin Bayelsa, Kogi da kuma Imo.

A ranar 11 ga watan Nuwamba ne aka shirya gudanar da zaɓukan gwamna a jihohin uku.

Ƴan takarar na jam’iyar APC sun haɗa da Hope Uzodimma wanda yake neman a sake zaɓensa a matsayin gwamnan jihar Imo, sai Timpre Sylva a jihar Bayelsa da kuma Usman Ododo wanda yake neman a zaɓe shi a matsayin gwamnan Kogi.

Tinubu ya yi kira da a gudanar da sahihin zaɓe ba tare da tahin hankali ba.

A yan kwanakin nan hukumar zaɓe mai zaman kanta ƙasa INEC ta nuna damuwarta kan yadda ake yawan samun rikice-rikice da ya shafi ƴan takara da kuma jam’iyunsu a jihohin uku

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya ƙirƙiri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a ƙara wa ƴan bautar ƙasa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...