Rahotanni daga Iran sun ce an samu fashewa a wata tankar dakon man Iran kusa da tashar ruwan Saudiyya a Jeddah.
Kafofin yada labaran Iran sun ce fashewar tankar ya haifar da tsiyayar mai a tekun Maliya.
Wata kafar talabijin din Iran Al Alam ta danganta fashewar da aikin ta’addanci.
Tankar mai suna Sinopa mallakin kamfanin man Iran ce.
Zuwa yanzu babu karin bayani kan ko akwai hasarar rayuka.