Sunshine da Pillars sun raba maki tsakaninsu | BBC Hausa Sport

Week 17

Hakkin mallakar hoto
NPFL

Sunshine Stars da Kano Pillars sun tashi 2-2 a wasan mako na 17 a gasar Firimiyar Najeriya da suka kara ranar Lahadi.

Anthony Omaka ne ya ci wa Sunshine kwallaye biyun, shi ma Auwalu Ali ne ya ci wa Pillars kwallayenta biyun.

Da wannan sakamakon Pillars ta hada maki 21, ita kuwa Sunshine tana da 27 kenan.

Pillars za ta karbi bakuncin Adamawa United a wasannin mako na 18, ita kuwa Sunshine Stars za ta ziyarci Heartland domin fafatawa a filin wasa na Okigwe Township stadium.

Sakamakon wasannin mako na 17:

  • Abia Warriors 1-0 Wolves
  • Katsina Utd 1-0 FC Ifeanyiubah
  • Akwa Utd 3-1 Heartland
  • Sunshine Stars 2-2 Kano Pillars
  • Adamawa Utd 2-1 Kwara Utd
  • MFM 0-0 Plateau Utd
  • Rivers Utd 0-0 Wikki
  • Lobi 2-1 Nasarawa Utd

Tun a ranar Asabar aka kara a wasa daya

Dakkada 2-0 Jigawa GS

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar Æ´an sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Ƴansanda sun kama wanda ya kitsa harin da aka kai wa jirgin ƙasa a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Alhamis, ta sanar da kame wanda ake zargin ya shirya harin da aka kai a jirgin ƙasan Abuja-Kaduna...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani É“angare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...