Sojoji ‘sun tursasa wa wasu ‘yan Kenya iyo a ruwan ba-haya’

Ruwan kwata

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Wasu ‘yan kasar Kenya sun shiga shafin Twitter don bayyana fushinsu kan wani rahoton da wata jaridar kasar, Standard Newspaper, ta wallafa cewa wasu sojoji sun ci zarafin wasu mazauna birnin Mombasa da ke bakin ruwa, a ranar Lahadi a lokacin da ake bukukuwan ranar gwarzaye.

An tsaurara matakan tsaro a birnin, a yayin da kasar ke bukukuwan wanda shugaban kasar, Uhuru Kenyatta, da wasu manyan kusoshin gwamnati suka halarta.

Jaridar ta wallafa rahoton da ke cewa an tursasa wa wasu mazauna birnin yin ninkaya a cikin ruwan ba-haya, yayin da kuma aka tursasa wa wasu zama a cikin tabo.

Wasu kuwa mazauna yankin sun yi zamansu ne a gida, saboda tsoron ka da sojoji su muzantasu, a cewar rahoton.

Sai dai kawo yanzu sojojin ba su ce komai ba game da zarge-zargen.

Wani matashi mai shekara 23 a duniya wanda ake kira Chikore, ya shaida wa jaridar cewa, yana kan hanyarsa ce ta zuwa wajen taron bikin lokacin da sojoji suka tsayar da shi saboda basu yarda da shi ba.

“Sun yi kokawa da ni har suka kaini kasa, daga nan kuma suka sa na yi iyo a cikin ruwan ba-haya. Na yi kokarin gudu amma sai suka buga mini gindin bindiga,” In ji shi.

Masu mu’amala da shafin Twitter sun bayyana wannan lamarin da cewa “abin kunya ne” kuma “abin kyama”:

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...