Sojoji sun kashe ‘yan ta’adda 7 a Kaduna

Dakarun sojojin Najeriya da ke aiki ƙarƙashin ‘Operation Whirl Punch’ sun yi nasarar kashe ‘yan ta’adda 7 a kauyen Kampanin Doka da ke karamar hukumar Birnin-Gwari a jihar Kaduna.

Wannan farmaƙin, wanda aka gudanar a matsayin martani ga hare-haren da ake kai wa al’ummar yankin, ya yi sanadin kakkaɓe ‘yan bindiga hudu a ranar 1 ga Nuwamba, 2023.

A cewar Laftanal Kanal Musa Yahaya, mukaddashin Daraktan hulda da jama’a na rundunar sojin Najeriya na Kaduna, sojojin tare da hadin gwiwar runduna ta daya ta Najeriya, sun yi gaggawar mayar da martani kan rahotannin hare-haren ‘yan bindiga a kauyen Kampanin Doka.

Rundunar ta kai ga ƙwato makamai da suka haɗa da bindiga kirar AK 47 guda daya, gidan harsasan AK 47 daya, adda daya, wayar hannu, da babura goma sha hudu da masu laifin ke amfani da su a baya.

More News

Dakarun Najeriya sun cafke wasu ƴan’aiken ƴanbindiga a Kaduna

Sojoji sun kama wasu mutum biyu da ake zargi da kaiwa 'yan bindiga sakonninsu a kasuwar ƙauyen SCC da ke ƙaramar hukumar Kachia a...

Ƴansanda sun hallaka masu garkuwa da mutane

Ƴansanda sun hallaka wasu masu garkuwa da mutane uku da ake zargin sun yi yunkurin yin garkuwa da matar wani dan majalisar dokokin jihar...

Ƴanbanga sun sake kawar da wani ƙasurgumin ɗanbindiga

Rahotanni da ke fitowa daga Arewa maso Yammacin Najeriya na nuna cewa an yi nasarar kawar da wani fitaccen dan bindiga a jihar Zamfara,...

Ƴansanda a Katsina sun yi nasarar cafke wasu tantiran masu safarar alburusai wa ƴanbindiga

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina a ranar Juma’a ta sanar da cewa ta kama wasu manyan ‘yan bindiga guda uku tare da kwato manyan...