Sojoji sun kashe ‘yan Boko Haram da mayakan ISWAP a Yobe

Rundunar sojin Najeriya ta ce a ci gaba da yaki da take da ” ‘yan ta’adda” a yankin arewa maso yammacin Najeriya, dakarun bataliya ta 120 da hadin gwiwar JTF sun kashe yan Boko Haram da mayakan ISWAP masu yawa da safiyar yau, a wani harin kwantan bauna da suka yi musu a kauyen Ngirbua da ke jihar Yobe.

A wata sanarwa da rundunar ta wallafa a shafukanta na sa da zumunta, rundunar ta ce dakarunta sun kashe mayaka da dama tare da kwace makamansu, amma sauran bayani kan abin da ya faru zai zo daga baya.

More News

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaƙi da yiwa tattalin arzikin ƙasa ne ya hana shi bayyana...