Sojoji sun kashe kwamandan Boko Haram Alhaji Modu da wasu mayaka 27

Dakarun rundunar sojan Najeriya dake yaki da yan ta’addan Boko Haram a yankin arewa maso gabas sun kashe Alhaji Modu daya daga cikin gawurtaccen mayakan Boko Haram.

A cewar Zagazola Makama wani masani kan yaki da yan ta’adda ya ce Modu wanda aka fi sani da Bem Bem an kashe shi tare da wasu mayakan kungiyar su 27.

Ya ce an kashe Modu ne ranar 3 ga watan Agusta a wani harin sojan sama a tsaunukan Mandara dake ƙaramar hukumar Gwoza.

A cewarsa bayanan sirrin da rundunar ta samu sun bayyana cewa mayakan na kungiyar ISWAP suna tattaruwa a yankin domin kai hari.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...