Sojoji sun kashe kwamandan Boko Haram Alhaji Modu da wasu mayaka 27

Dakarun rundunar sojan Najeriya dake yaki da yan ta’addan Boko Haram a yankin arewa maso gabas sun kashe Alhaji Modu daya daga cikin gawurtaccen mayakan Boko Haram.

A cewar Zagazola Makama wani masani kan yaki da yan ta’adda ya ce Modu wanda aka fi sani da Bem Bem an kashe shi tare da wasu mayakan kungiyar su 27.

Ya ce an kashe Modu ne ranar 3 ga watan Agusta a wani harin sojan sama a tsaunukan Mandara dake ƙaramar hukumar Gwoza.

A cewarsa bayanan sirrin da rundunar ta samu sun bayyana cewa mayakan na kungiyar ISWAP suna tattaruwa a yankin domin kai hari.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) Æ™arÆ™ashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da Æ™arar da É—an majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]