Sojoji sun kashe ƴan bindiga 7 a Kaduna

Sojojin rundunar samar da tsaro ta Operation Safe Haven sun kashe yan bindiga 7 tare da gano makamai a ƙaramar hukumar Zangon Kataf ta jihar Kaduna.

A wata sanarwa ranar Talata mai magana da yawun rundunar, Kyaftin Oya James ya ce sojojin dake gudanar da sintiri sun yi arba da yan bindigar ne a wurin da ake kira tudun Kachalla inda aka yi musayar wutar da ta kai ga kisan ƴan bindiga shida a yayin da wasu suka tsere da raunin harbin bindiga.

Sanarwar ta ce an gano bindigar AK-47, harsashi masu yawa, waya kirar Tecno, babur da sauran abubuwa biyo bayan binciken wurin da aka yi artabun da sojoji suka yi.

Ya kara da cewa sojojin sun kuma kashe wani sanannen dan bindiga da ake kira da Musa Wada a ƙauyen Kondo dake ƙaramar hukumar.

Sanarwar ta cigaba da cewa mutane 33 da ake zargi da aikata laifuka daban-daban aka kama a cikin makon da ya wuce.

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya ƙirƙiri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a ƙara wa ƴan bautar ƙasa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...