Sojan Saman Najeriya Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane Sama Da 30 A Kaduna

Dakarun sojan sama na rundunar samar da tsaro ta Operation Whirl Punch sun kashe yan fashin daji masu garkuwa da mutane da basu gaza 30 ba a wani harin sama da suka kai a wajejen Kwiga zuwa Kamfanin Doka dake karamar hukumar Birnin Gwari ta jihar Kaduna.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da daraktan hulÉ—a da jama’a na rundunar sojan saman Najeriya, AVM Edward Gabkwet ya sanar ranar Litinin a Abuja.

Gabkwet ya ce an kai harin ne biyo bayan bayanan sirri da aka samu na ganin gungun wasu yan bindiga a yankin.

Ya ce bayanan sirrin da aka samu ya nuna cewa yan ta’addar sune dai suka kai wa sojoji harin kwanton É“auna a Kwanar Mutuwa ranar 27 ga watan Janairu da kuma wasu hare-hare da kuma garkuwa da mutanen da basu ji basu gani ba a Birnin Gwari.

More News

Ƴan Fashin Daji Sun Kashe Mutane 7 A Jihar Kebbi

Mutane 7 aka bada rahoton ƴan fashin daji sun kashe  a garin Tudun Bici dake ƙaramar hukumar Danko Wasagu ta jihar Kebbi. A cewar mazauna...

Tsoffin gwamnoni sun wawashe sama da naira tiriliyan 2 tun komawa dimokuraÉ—iyya

Aƙalla tsoffin gwamnoni 58 ne ake zargin sun wawure kuma sun yi almubazzarancin jimillar naira Tiriliyan 2.187 a cikin shekaru 25 tun komawa mulkin...

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar Æ´an sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...