Shin ka san wane ne marigayi Justice Mamman Nasir?

FACEBOOK/AMINU GAMAWA

Hakkin mallakar hoto
FACEBOOK/AMINU GAMAWA

An haifi Justice Mamman Nasir a jihar Katsina a shekarar 1929.

Ya yi karatun sakandare dinsa a Kwalejin Kaduna inda ya samu takardar shaidar kammala karanun sakandare ta WAEC a 1947.

Daga bisani ya tafi jami’ar Ibadan inda ya samu digiri a harshen Latin.

Daga nan kuma ya tafi makarantar horar da lauyoyi inda ya samu digiri a bangaren shari’a a 1956 kuma a wannan shekarar ce aka rantsar da shi a matsayin cikakken lauya a wata kotu da ke Ingila da ake yi wa lakabi da ‘Licoln Inn.”

Ya dawo Najeriya a 1956 a matsayin lauya mai shigar da kara.

A 1961, an nada shi Ministan Shari’a na Arewacin Najeriya inda ya shafe shekaru biyar kan mukamin sai kuma daga baya ya zama darakta a ofishin lauyoyi masu shigar da kara na arewacin Najeriya a 1967.

A 1967 din dai Mamman Nasir ya zama babban lauya a ma’aikatar shari’a a jihar arewa ta tsakiya a wancan lokaci.

Ya rike wannan mukamin na shekaru bakwai inda daga nan ne aka nada shi alkalin kotun koli a 1975.

An kuma nada shi a matsayin shugaban kotun daukaka kara, mukamin da ya rike kenan har zuwa 1992 inda daga nan ne ya zama Galadiman Katsina.

An nada shi a matsayin Galadiman Katsina a ranar 9 ga watan Mayun 19992.

Ya kuma rasu ranar Asabar 13 ga watan Afrailun 2019.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...