Sheikh Giro ya nemi afuwar ‘yan Najeriya game da tsine wa “makiyan” Buhari

Malamin Izala a Najeriya, Shiek Abubakar Giro Argungu, ya nemi afuwar ‘yan Najeriya a kan wani bidiyo da yake nuna malamin yana kakkausan kalamai a kan “makiya” Shugaban kasar Muhammadu Buhari.

Malamin ya bayyana cewa bidiyon an nade shi ne tun a 2015 kuma ya yi kalaman ne sakamakon wata matsala da ta faru a siyasar wancan lokaci.

Bidiyon dai ya nuna Malamin yana kwashewa marasa goyon bayan Buhari albarka sa’annan ya yi wa marasa ci gaban Najeriya fatan hatsarin mota.

Sheik Abubakar ya ce ya yi nadamar yin wadannan kalamai kuma ya amince da kuskurensa.

Malamin ya ce a wancan lokaci ya yi raddi ne ga wata kabila mai suna ‘yan tatsine.

Tun bayan da guguwar siyasar 2019 ta fara kadawa a Najeriyar aka samu rarrabuwar kai na malamai musamman na Izala a kasar.

A kwanakin baya an samu sabanin ra’ayi da Sheik Ahmed Gumi wanda daya daga cikin Malaman Izala ne a kasar.

Haka a wani bangaren an samu sabanin ra’ayi da Shiek Yusuf Sambo Rigachikun bayan ya bayyana ra’ayinsa na goyon bayan dan takarar jam’iyyar PDP Atiku Abubakar.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...