Shehu Sani na son matar El-Rufai ta daina magana akan gashinsa

Shehu Sani, sanata dake wakiltar mazabar Kaduna ta tsakiya ya nemi gwamna Nasiru el-Rufa’i da jawa matarsa kunne kan yadda take yawan magana akan gashin kansa.

A wani sako da ya wallafa a shafinsa na Facebook sanatan ya ce matar gwamnan, Hadiza el-Rufai ko da yaushe tana magana akan gashin kansa a duk lokacin da ta fita yakin neman zabe.

Hadiza wacce mawallafiyar littafai ce ta kasance akan gaba-gaba wajen yakin neman zaben mijinta gabanin zaben gwamnan da za a gudanar ranar cikin watan Maris.

“Ina rokon Gwamna da ya gargadi matarsa da ta daina magana akan gashina a duk sa’ilin da taje yakin neman zabe.Duk inda taje maganar bata wuce ta gashina.Ba laifina bane idan mijinta bashi da arzikin gashi.Na dauki abin da take a matsayin kalaman batanci,zan kai kararta wurin Sheikh Gummi ko kuma majalisar Limamai. Haba jama’a,” a cewar sakon.

Wannan ne dai karo na farko da sanatan yayi musayan yawu da matar gwamnan.

More News

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miĆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaĆ™i da yiwa tattalin arzikin Ć™asa ne ya hana shi bayyana...