Shafin YouTube ya janyo wa wani daurin shekara 4

An kama Muhammed Sekkaki da laifin yin kalaman batanci ga sarki Muhammad VI, da kiran 'yan kasar jakai

An yanke wa fitaccen mai wallafa bidiyo a shafin YouTube dan Morocco hukuncin zaman kaso na shekara 4 da tarar dala 4,000, bayan an same shi da yin kalaman batanci ga sarkin kasar.

A farkon wannan watan ne aka kama Muhammed Sekkaki sakamakon sukar Sarki Muhammad a wani jawabi da ya yi, tare da kiran ‘yan Morocco da jakai.

Sai dai ya na shirin daukaka kara kan hukuncin da aka yanke masa.

A wani hukuncin na daban, an daure dan jarida kuma mai fafutuka Omar Radi kan laifin wallafa sakon Twitter da ya zagi wani alkali a watan Afirilu da ya wuce.

Lauyansa ya ce za a ci gaba da tsare shi har sai ranar biyu ga watan Janairu inda za a gurfanar da shi gaban shari’a.

Kungiyoyin kare hakkin bil adama a Morocco sun nuna damuwarsu kan yadda ake matsa wa mutane, musamman idan sun fadi albarkacin bakinsu kan wani abu da ya shafi masu mulkin kasar.

Tun bayan kadawar guguwar sauyi a yankin gabas ta tsakiya a shekarar 2011, Sarki Muhammad VI, ya raba madafun iko tsakanin fadarsa da zababbiyar gwamnatin kasar.

Sai dai masu sharhi kan al’amura na cewa har yanzu yana da karfin fada aji da zartar da hukunci na karshe a kan muhimman batutuwa a kasar.

More News

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miĆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaĆ™i da yiwa tattalin arzikin Ć™asa ne ya hana shi bayyana...